Skip to content
Home » Hausa Hymns » Ruhun iko, zo gare mu, Mun ga kasawarmu yau

Ruhun iko, zo gare mu, Mun ga kasawarmu yau

    Verse 1
    Ruhun iko, zo gare mu,
    Mun ga kasawarmu yau.
    Rashin jinkai, rashin kauna
    Rashin musun kanmu ma.

    Chorus
    Sai ka zo, ka tsarkake mu
    Daga dukan kasawa.
    Muna jira, muna jira
    Tsarkake mu duk yanzu.

    Verse 2
    Ruhun sani, zo gare mu,
    Akwai duhu cikinmu.
    Sanasshe mu, koya mana
    Hanyar tsarkakewar rai.

    Verse 3
    Ruhun wuta, zo gare mu,
    Kone duk muguntarmu
    Har mu zama mutanenka,
    Cikin dukan gaskiya.

    Verse 4
    Ruhun haske da addu’a,
    Bi da mu, ka karfafa.
    Muna bege, muna bege
    Har mu sami nasara.

    Verse 5
    Ruhun kauna, zo gare mu,
    Sai ka yafe mu yanzu.
    Muna jira, muna kuka,
    Amsa dai addu’armu.

    Verse 6
    ‘Yanuwa, ku yafa Yesu,
    Yafa sabon hali kuwa
    Yafa kuma zuciyar tausayi,
    Ladabi da jurewa.

    Verse 7
    Ruhun Kristi, ni na gode,
    Kana nan a zuciya,
    Mallake ni, mallake ni
    Daga yau har abada.

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *